Hukumar Shige da Fice ta Najeriya ta daga darajar jami’anta 7,000

Hukumar Shige da Fice ta Kasa (NIS) karkashin jagorancin Kwanturola Janar Wuraola Adepoju ta daukaka darajar jami’anta kusan 7,000.

Jawqbin hakan, na kunshe ne a cikin wata takarda mai dauke da sa hannun sakataren hukumar, Alhaji Jafaru Ahmed.

A jawabinta ga Jami’ai da Ma’aikatan Hukumar a lokacin faretin wata-wata, hukumar ta bukaci da su fifita martabar aikin fiye da bukatun kashin kansu domin hukumar na daya daga cikin manyan hukumomin da alhakin kare dukiyoyin al’umma ya rataya a wuyansu.

Sannan ta yi alkawarin ba da fifikon jin dadin ma’aikata, tare da shan alwashin cewa daga yanzu dole ne a yi wa manyan jami’ai karin girma domin abin takaici ne ganin yadda wasu tsofaffin jami’ai suka dade a mataki daya.

Post masu alaƙa

Kwalejin sojan ruwa dake Dawakin-Tofa ta kara karfafa hadin gwiwar aiki tare da rundunar yan sandan Kano.

Sojojin Najeriya sun ceto mutane 9 daga masu garkuwa a Kogi.

Kotu tsare mutane biyu da ake zargi da rushe Gadar Watari da yanka filaye ba bisa ka’ida ba a Kano.