Home » Isra’ila Na Shan Caccaka Kan Hana Shiga Da Abinci Gaza

Isra’ila Na Shan Caccaka Kan Hana Shiga Da Abinci Gaza

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Daga: Rabi’u Hashim Rabi’u

Ƙasar Isra’ila na ci gaba da shan suka mai zafi daga bangarori daban-daban na duniya bayan sanar da katse duk nau’in tallafi daga shiga zirin Gaza.

Matakin na Isra’ila ya zo ne a daidai lokacin da ake matukar bukatar kayan abinci saboda azumin watan Ramadan.

Kasashen da suka shiga tsakani wajen ganin an tsagaita wuta Qatar da kuma Masar sun zargi Isra’ilar da saba yarjejeniyar ta tsagaita wuta da aka sanya wa hannu tare da amfani da yunwa a matsayin makamin yaki.

EU ta bukaci dakatar da farmakin Isra’ila a yamma da kogin Jordan

Kashin farko na yarjejeniyar ya bada damar an rika shigar da kayan agaji zirin bayan shafe watanni ana fama da bukatarsu musamman ma magunguna da abinci ba tare da samu ba.

Kungiyar Hamas ta zargi Isra’ila da kokarin kauce wa kashin farko na yarjejeniyar tsagaita wutar bayan ya kare a ranar Asabar.

Isra’ila ta bukaci tsawaita yarjejeniya har bayan Ramadan

Isra’ila ta yi ikirarin cewa wani sabon kudurin Amurka ya bukaci a tsawaita kashin farko na yarjejeniyar sakamakon Ramadan maimakon shiga kashi na biyu wanda da zarar an fara shi babu koma wa yaki.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?