Jami’ar Ahmadu Bello, ABU, Ta Sanar da Fara Zangon Karatu Na 2

Majalisar Gudanarwa ta Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, ta sanar da sake bude makarantar domin ci gaba da gudanar karatun zango na biyu.

A wata sanarwa da jami’ar ta fitar, ta ce sakamakon taron gaggawa karo na 523 da majalisar ta gudanar a jiya Juma’a 16 ga watan Yuni 2023,

 Rajotanni sun bayyana cewa daliban jami’ar sun shafe tsawon wata guda suna zaman gida sakamakon yanke wutar lantarki da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki ta Kaduna KEDCO ta yi a jami’ar.

Binciken da aka gudanar, ya tabbatar da dawowar wutar lantarkin, lamarin da ake zargin shi ne ya sa aka yi wa daliban kiranyen dawowa jami’ar.

Sai dai takardar sanarwar bata fayyace ko hukumar jami’ar ta samu nasarar biyan kudaden wutar lantarkin da ake binta ko kuma irin matsayar da suka samu da hukumar samar da wutar lantarkin don kaucewa faruwar irin haka a nan gaba.

Yanzu dai ana sa ran daukacin dalibai za su dawo a ranar Litinin don ci gaba da gudanar da karatu bisa tsarin yadda aka yi wa jadawalin karatun kwaskwarima.

Post masu alaƙa

Babandede Ya Ziyarci Iyalan Hon. Laushi, Ya Ba Su Tallafi

Da Fulani Aka Kama da Wuraren ƙera Makamai a Filato, da War Haka Duniya ta Dauka:-Zagazola Makama

Gwamna Bala Mohammed ya canja sheka daga jam’iyar PDP zuwa jam’iyyar APM