Home » Kanfanonin kasar Jamus na shirin zuba hannun jari a Najeriya

Kanfanonin kasar Jamus na shirin zuba hannun jari a Najeriya

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Kanfanonin kasar Jamus na shirin zuba hannun jari a Najeriya

Hukumar Bunƙasa Zuba  hannun Jari ta Ƙasa, NIPC, ta ce suna haɗa kai da masu saka hannun jari daga ƙasar Jamus domin bunƙasa kasuwanci a tsakanin ƙasashen biyun.

Babbar Sakatariyar hukumar, Aisha Rimi, ce ta bayyana hakan a Abuja a yayin wata tattaunawa da wasu kamfanoni 22 daga ƙasar Jamus da Yammancin Turai waɗanda suka nuna sha’awarsu ta zuba hannun jari a ƙasar nan.

Kuma ana sa ran za su zuba kuɗin da zai kai yuro miliyan dubu uku.

Sakatariyar ta ce sun tattauna da masu ruwa da tsaki a jihohin ƙasar nan domin tattara bayanai game da ɓangarorin da za su samar da riba tare da miƙa bayanan ga masu son zuba hannun jarin.

Shi ma shugaban masu son zuba hannun a Najeriya daga ƙasar Jamus, Michael Schmidt, ya ce sama da kamfanoni 22 ne suka ziyarci jihohi daban-daban na ƙasar nan waɗanda kuma tuni suka nuna sha’awarsu ta zuba hannun jari a ɓangarori daban-daban na kasuwanci a ƙasar nan.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?