Home » Kano: Wata kotu ta hana a kama Musa Iliyasu Kwankwaso

Kano: Wata kotu ta hana a kama Musa Iliyasu Kwankwaso

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Kano: Wata kotu ta hana a kama Musa Iliyasu Kwankwaso

Babbar kotun tarayya dake zaman ta a jihar Kano ta bada umarnin hana kama dan siyasar nan wato Musa Iliyasu Kwankwaso.

Tun bayan da kotun sauraren kararrakin zaben gwamnan kano ta ce Nasiru Gawuna ne gwamnan Kano ba Abba Kabir Yusuf ba, Musa Iliyasu Kwankwaso yake yiwa gwamnatin bankada tare da yin wasu zarge-zarge ciki har da shirin gwamnatin na  ranto kudade, domin ta tafi ta bar su da biyan bashi.

Musa Iliyasu Kwankwaso ne dai ya shigar da karar gwamnatin jihar kano da kwamishinan yan sanda na jihar kano, tare da rokon kutun da ta hana wadanda yake kara kama shi har sai kotun ta ji bahasin dalilin da yasa suke son kama shi.

A cikin Umarnin kotun mai kwanan watan 25 ga watan October, 2023, Kotun ta bukaci wadanda ake kara da kada su kama mai Kara (Musa Iliyasu Kwankwaso), sannan kowa ya tsaya a matsayinsa har sai kotun ta sauraren dukkanin bangarorin Shari’ar.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?