Home » Iyalan sojojin Najeriya za su rabauta da samun tallafin biliyoyin kudi

Iyalan sojojin Najeriya za su rabauta da samun tallafin biliyoyin kudi

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Iyalan sojojin Najeriya za su rabauta da samun tallafin biliyoyin kudi

Shugaba Bola Ahmad Tinubu ya amince Gwamnatin Tarayya ta biya Naira biliyan 18 ga Asusun  Group Life Assurance  domin raba wa ga iyalan sojojin da suka kwanta dama, wajen kare ƙasar nan.

Sojojin Najeriya da dama sun rasa rayukan su ne a yaƙe-yaƙen kare ƙasar nan daga Boko Haram, ‘yan bindiga da masu tayar da ƙayar bayan neman ɓallewa daga Najeriya, wato IPOB da ke Kudu maso Gabas.

Tinubu ya bayar da wannan albishir ne yayin ƙaddamar da Gidauniyar Tallafa Wa Iyalan Sojojin da Suka Kwanta Dama, a wurin Ranar Tunawa da Mazan Jiya ta 24, a Fadar Shugaban, a Abuja.

Ya ce har yau akwai ɗimbin bashin da ke kan gwamnati  na yi wa waɗannan mazan jiya godiya da sakayya, waɗanda suka sadaukar da kan su wajen tsaron ƙasar nan.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?