Karamin Ministan Albarkatun Man Fetur Na Najeriya Ya Yi Murabus

Karamin ministan albarkatun man fetur na Najeriya Timipre Sylva ya yi murabus daga mukaminsa domin neman sabon wa’adi a matsayin gwamnan jihar Bayelsa mai arzikin man fetur a yankin Neja Delta.

Wasu majiyoyi a ma’aikatarsa da suka bukaci a sakaya sunansu ne suka shaida wa majiyarmu a jiya.

Murabus din Sylva na zuwa ne kwanaki 60 kacal, kafin wa’adinsa a kan mukamin karamin ministan albarkatun mai ya kare kuma a daidai lokacin da ake shirin kafa sabuwar gwamnati a Najeriya,

Rahotanni sun tabbatar da cewa, ministan ya mika wa shugaba Buhari kuma babban ministan albarkatun man fetur takardar murabus dinsa tun a makon da ya gabata, kuma tuni ya daina zuwa ofishinsa, a cewar wata majiya da ta bukaci a sakaya sunanta.

Haka kuma, wata majiya tabbatar da cewa ƙaramin ministan na neman tikitin takarar gwamnan jihar Bayelsa a ƙarkashin inuwar jam’iyyar APC mai mulki a zaben fidda gwani na jam’iyyar da aka shirya gudanarwa a ranar 14 ga watan Afrilun mai zuwa.

A watan Agustan shekarar 2019 ne aka nada Sylva a matsayin karamin ministan albarkatun man fetur, inda ya jagoranci manyan sauye-sauye a fannin mai wadanda suka hada da zartar da dokokin da suka yi wa tsarin kasafin kudin sashen kwaskwarima a wani yunkuri na karfafa masu zuba hannun jari guiwa.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr