Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ya bai wa wata matashiyam mai suna Joy Ogah aron kujerarsa na kwana ɗaya.
Wannan lamari ya faru ne a fadar shugaban ƙasa, yayin da Shettima ya karɓi bakuncin wani tawagar PLAN International karkashin jagorancin shugabar tawagar, Helen Mfonobong Idiong.
A cikin jawabin sa, Shettima ya jaddada ƙudirin gwamnatin shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu na inganta karatun yara mata a fadin Najeriya.
Ya bayyana cewa gwamnati za ta ci gaba da haɗin gwiwa da PLAN International domin ganin shawarwarin da suka bayar kan ilimin yara mata sun samu karɓuwa da aiwatarwa.
Ya bayyana cewa ci gaban yara mata babban ginshiƙi ne na cigaban ƙasa baki ɗaya.
A ɓangarenta, matashiyar Joy Ogah ta yi godiya da wannan damar, inda ta ce mata na iya zama shugabanni idan hukumomi da masu ruwa da tsaki suka aiwatar da matakan da suka dace.