Home » An Kawo Karshen Takkadamar Masallacin Sheikh Bin Uthman

An Kawo Karshen Takkadamar Masallacin Sheikh Bin Uthman

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Daga: Fatima Muhammad Adam 

Majalisar Malamai Ta Jihar Kano Ta Yanke Hukunci Kan Rikicin Masallacin Sheikh Bin Uthman (Sahaba) Dake Kundila Karamar Hukumar Tarauni A Jihar Kano. 

Shugaban majalisar malamai ta Kano Sheikh Ibrahim Khalil ya bayyana cewa bayan zama da dukkanin ɓangarorin da danbarwar sabon Masallacin Sahaba dake Kundila, majalisar ta yanke hukunci na ƙarshe a kan dambarwar.

”Mun yanke hukuncin Sheikh Muhammad Bn Othman zai koma Masallacin da na Sahaba, shi kuma Mai Kifi da sauran mutanensa za su cigaba da riƙe na su Masallacin na Jami’urrahman.”

Malam Ibrahim Khalil ya bayyana hakan ne lokacin da yake bayyana sakamakon zaman da suka yi ga manema labarai a Kano.

Ya ce Sheikh Muhammad Bin Othman ya amince zai cigaba da jagorantar Sallah a tsohon masallacinsa na Sahaba dake Kundila, yayin da su kuma su Mai Kifi za su cigaba da gudanar da harkokin Masallacin su na Jami’urrahman.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?