Home » Katsina: Hukumar NDLEA Ta Bankaɗo Gonaki 3 Da Ake Noma Tabar Wiwi

Katsina: Hukumar NDLEA Ta Bankaɗo Gonaki 3 Da Ake Noma Tabar Wiwi

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Hukumar da ke yaki da miyagun kwayoyi a Najeriya NDLEA ta gano gonaki uku da ake shuka ganyen wiwi a jihar Katsina.

Mataimakin shugaban hukumar mai kula da harkokin gudanarwa a jihar, Halilu Hamidu ne ya tabbatar da wannan nasara bayan samun bayanai daga wasu mutane.


Hamidu ya ce wannan shi ne karon farko da hukumar ta gano irin wannan gonar a ƙauyen Sobashi na karamar hukumar Dutsi.

Ya bayyana cewa masu waɗancan gonaki suna amfani da su ne wajen shuka tabar ta wiwi ta hanyar fakewa da noman kayan lambu irinsu tattasai da tumatur.

Jami’in ya ƙara da cewa hukumar ta kama mutum ɗaya sannan tana bibiyar sawun sauran abokan huldarsa.

 A cewar hukumar wannan shi ne karon farko da ta gano gonakin shuka wiwi masu yawa a jihar ta Katsina.

Sannan hukumar ta kama sinadarin Kodin da darajarsu ta kai Naira miliyan goma.

NDLEA ta kara da cewa ba karamin hadari wadannan miyagun kwayoyin suke da su ba ga al’umma

Katsina na daya daga cikin jihohin Najeriya da ke iyaka da Jamhuriyar Nijar, inda masu fasaƙwaurin haramtattun kayayyaki ke safararsu a tsakanin kasashen biyu wanda hakan a ya sa hukumin ƙasar Nijar kokawa a kwanakin baya.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?