Kungiyar ECOWAS za ta yi taron gaggawa kan juyin mulki a kasar Nijar

A gobe Lahadi shugabannin Yammacin Afrika za su gudanar da wani taron gaggawa don tattaunawa kan juyin mulki da aka yi a Jamhuriyar Nijar a ranar Laraba.

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu kuma sabon shugaban kungiyar ta ECOWAS, shi ne zai jagoranci zaman na ranar Lahadi wanda za a yi a Abuja, babban birnin Tarayyar Najeriya.

Shugaba Tinubu ya yi Alla-wadai da juyin mulkin a cikin wata sanarwa inda kuma ya yi wa al’ummomin kasashen waje alƙawarin cewa zai yi iyakacin ƙoƙarinsa domin kare dimokuraɗiyya da kuma tabbatar da ɗorewar kyakkyawan shugabanci a yankin.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr