• Home  
  • Lakurawa Sun Tada Bam A Zamfara- Police 
- Babban Labari - Labarai

Lakurawa Sun Tada Bam A Zamfara- Police 

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta ce kungiyar ‘yan ta’addar Lakurawa ne suka tayar da bama-bamai a wasu kauyuka biyu na gundumar Dansadau a karamar hukumar Maru.  

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta ce kungiyar ‘yan ta’addar Lakurawa ne suka tayar da bama-bamai a wasu kauyuka biyu na gundumar Dansadau a karamar hukumar Maru.  

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Zamfara CP Muhammad Shehu Dalijan ne ya bayyana hakan a wata zantawa da manema labarai ta wayar tarho.

CP Muhammad ya tabbatar da tashin bama-baman a kauyen ‘Yar Tasha da ke kan hanyar Dansadau.

Kwamishinan ya ce tashin bama-baman ya yi sanadaiyyar mutuwar mutum daya, yayin da wasu uku suka samu raunuka daban-daban.

An ce bama-baman da ake zargin ‘yan ƙungiyar ta’addar Lakurawa da dasa wa sun tashi da misalin karfe 8 na safiyar ranar Laraba.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai