Home » Lakurawa Sun Tada Bam A Zamfara- Police 

Lakurawa Sun Tada Bam A Zamfara- Police 

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta ce kungiyar ‘yan ta’addar Lakurawa ne suka tayar da bama-bamai a wasu kauyuka biyu na gundumar Dansadau a karamar hukumar Maru.  

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Zamfara CP Muhammad Shehu Dalijan ne ya bayyana hakan a wata zantawa da manema labarai ta wayar tarho.

CP Muhammad ya tabbatar da tashin bama-baman a kauyen ‘Yar Tasha da ke kan hanyar Dansadau.

Kwamishinan ya ce tashin bama-baman ya yi sanadaiyyar mutuwar mutum daya, yayin da wasu uku suka samu raunuka daban-daban.

An ce bama-baman da ake zargin ‘yan ƙungiyar ta’addar Lakurawa da dasa wa sun tashi da misalin karfe 8 na safiyar ranar Laraba.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?