Rundunar ƴan sandan jihar Zamfara ta kama wanda ake zargi da safarar Alburusai a tankin Babur
Rundunar ƴan sandan jihar Zamfara ta sanar da kama wani mutum mai suna, Umar Sani mai shekaru 30 ɗauke da alburusai guda 100 masu rai na bindiga ƙirar AK-47 a jihar. Kakakin rundunar jihar Zamfara, DSP Yazid Abubakar,ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a ranar asabar. Sanarwa ta […]










