Home » Mawaki El’Muaz Birniwa Ya Rasu

Mawaki El’Muaz Birniwa Ya Rasu

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Allah Ya yi wa fitaccen mawaƙin Hausa El’Muaz Birniwa rasuwa a ranar Laraba da yamma sakamakon bugun zuciya.

Rahotanni sun tabbatar da cewa Elmuaz ya rasu ne sakamakon bugun zuciya a lokacin da yake halartar bikin abokin sana’arsa mawaƙi Auta Waziri.

Falalu Dorayi ya shaida wa TRT Afrika Hausa cewa “An je ƙwallo irin ta aure ɗin nan wasu ma sun ce ba a gama ta ba sai ya ce jiri na kwasarsa, daga haka sai ya faɗi. Aka ɗauke shi aka wuce da shi asibiti a nan Kaduna, to bayan kamar awa guda ne asibitin suka ba da sanarwar cewa Allah Ya yi masa rasuwa,” 

Elmuaz ya kasance mawaƙi, marubucin waƙoƙi, furodusan fina-finai, kuma shi ne mataimakin ƙungiyar mawaka ta Murya Daya.

Elmuaz na yin waƙoƙin jan-hankali da wa’azantarwa da kuma na siyasa.

Ana sa ran za a yi jana’izarsa a ranar Alhamis da misalin ƙarfe 1 na rana a Kaduna.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?