Home » Mahaifiyar Gwamnan Jigawa ta rasu

Mahaifiyar Gwamnan Jigawa ta rasu

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Allah Ya yi wa mahaifiyar Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, Hajiya Maryam Namadi, rasuwa da safiyar ranar Laraba, 25 ga watan Disamba, 2024.

Babban Sakataren Yaɗa Labaran Gwamnan, Hamisu Mohammed Gumel ne ya bayyana hakan a ranar Laraba.

Ya ce, za a yi jana’izarta da misalin ƙarfe 4:30 na yamma a garin Kafin Hausa.

Gwamnan, da iyalansa sun buƙaci ɗaukacin Musulmi da su yi mata addu’ar samun rahama daga Allah.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?