Majalisar Dinkin Duniya Ta Yi Gargaɗi Game da Munin Yakin Ƙasar Sudan

Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya bayyana tashin hankalin da ke faruwa a Sudan a matsayin abin takaici, inda ya gargadi taron Majalisar a jiya Talata cewa yakin na iya yaduwa zuwa wasu kasashen yankin.

A halin da ake ciki wani jirgin ruwa dauke da fararen hula 1,687 daga kasashe fiye da 50 da suka tsere daga rikicin Sudan ya isa kasar Saudiyya, kamar yadda ma’aikatar harkokin wajen kasar ta bayyana, wanda shi ne aikin ceto mafi girma da masarautar Gulf ta yi a halin yanzu. Sanarwar ta ce, kawo yanzu an kwashe mutane 2,148 zuwa masarautar daga Sudan, ciki har da baki fiye da 2,000.

Post masu alaƙa

CP Bakori ya umarci kwamandojin yan sanda su ƙara kaimi wajen yaki da laifuka a Kano.

KACRAN: Babu wani babban rikicin manoma da makiyaya a Yobe

CP Ibrahim Bakori ya kai gaisuwar ban-girma ga Sarkin Karaye tare da halartar bikin rantsar da yan NYSC.