Majalisar Zartarwa ta Jigawa ta Amince da Fitar da Naira Biliyan 3.2 Domin Noma da Ƙarfafa Matasa

Majalisar Zartarwa ta Jihar Jigawa ta amince da fitar da sama da naira biliyan 3.2 domin aiwatar da shirye-shiryen bunkasa harkokin noma da kuma ƙarfafa matasa a fadin jihar.
Kwamishinan Yada Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na jihar, Honarabul Sagir Musa, ne ya bayyana hakan yayin da yake yi wa manema labarai bayani kan sakamakon taron majalisar.
Ya ce daga cikin adadin kudaden da aka amince da su, an ware naira biliyan 1.575 domin biyan kaso 30 cikin 100 na kudin sayen famfunan ban ruwa guda 35,000, wadanda za a raba wa manoma a dukkan kananan hukumomi 27 na jihar.
Hon. Sagir Musa ya bayyana cewa famfunan ban ruwan da ke aiki da fetur za su taimaka wajen inganta aikin noman rani, tare da ƙarfafa matasa su rungumi noma a matsayin sana’a da kasuwanci.
Haka kuma, kwamishinan ya kara da cewa majalisar ta amince da kashe naira biliyan 1.649 domin sayen murhunan dafaffen shinkafa guda 52 da kuma na’urorin busar da amfanin gona masu amfani da hasken rana guda 13, domin rabawa matasa a matsayin shirin ƙarfafawa.
Ya ce kayan aikin, ciki har da na’urorin sarrafa shinkafa, za su taimaka wajen inganta sarkar darajar noma, samar da ayyukan yi, da kuma rage talauci a jihar.
Bugu da ƙari, Hon. Sagir Musa ya bayyana cewa majalisar ta kuma amince da kashe naira miliyan 240.6 domin sayen kayan ofis ga wani shiri da Bankin Duniya ke tallafawa mai suna Sustainable Power and Irrigation for Nigeria.
Ya ce dukkan wadannan amince-amince da shirye-shiryen suna cikin manufofi maki 12 na Gwamna Malam Umar Namadi, musamman bangaren inganta noma da amfani da injina a harkokin noma.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *