Mai bai wa Shugaba Bola Tinubu shawara kan harkokin sadarwa Daniel Bwala, ya ce akwai wasu muradan ƙasashen waje da ke taka rawa wajen ƙara ta’azzarar matsalar rashin tsaro a Najeriya.
Da yake magana a shirin The Link Up Podcast na Echoo Room, Bwala ya ce ɗaya daga cikin manyan abubuwan da ke haddasa matsalar shi ne ayyukan ta’addanci a ƙasashen yankin Sahel da ke makwabtaka da Najeriya.
A cewarsa, ‘yan ta’addan kan kai hare-hare a cikin Najeriya kafin su tsallaka zuwa ƙasashen da suka fito.
Bwala ya kuma yi zargin akwai wasu mummunan nufi daga ƙasashen waje da ke aiki a kan Najeriya. Ya ce tun lokacin da Boko Haram ta fara kai hare-hare a Jihar Barno, wasu ƙungiyoyin agaji na ƙasashen waje sun yi hayar gidaje na tsawon shekaru 10 zuwa 15, lamarin da ya ce ya haifar da tambayoyi kan dalilin yin irin wannan shiri na dogon lokaci.
Ya ƙara da cewa a lokuta da dama sojojin Najeriya sun kama wasu da ake zargin ‘yan Boko Haram ne, inda aka samu baƙi ‘yan ƙasashen waje a cikinsu.
A cewarsa, irin waɗannan abubuwa na ƙara rura wutar matsalar tsaro tare da sanya kawo ƙarshenta ya zama mai wahala.
Sai dai ya ce hukumomin soji ba sa bayyana ƙasashen da waɗanda aka kama suka fito saboda dalilan tsaro
