Majalisun Najeriya Sun Amince da dokar hukunta masu lalata da ɗalibai a Jami’o’i

Majalisar Wakilan Najeriya karo ta 9 ta amince da ƙudirin dokar da zai haramtawa tare da hukunta duk malamin da aka samu da laifin cin zarafi ko lalata da ɗalibai a kwalejoji da jami’o’i a ƙasar nan.

Tun a shekarar 2020 Majalisar Dattawa ta amince da ƙudirin mai taken Ba da Kariya da Haramtawa da Hukunta Haike Wa Ɗalibai a Manyan Makarantu wanda ke ɗauke da ƙunshe- ƙunshen hukunci daban-daban.

Shugaban kwamatin Majalisar Dattawa kan harkokin shari’a, Sanata Opeyemi Bamidele, ya ce taron gamayyar ‘yan majalisar ya haɗe kan tanade-tanaden biyu kafin ya gabatar da rahotonsa a zauren Majalisar da aka yi a jiya.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr