Home » “Maslahar Al’umma Gwamnati Ta Duba Kafin Rufe Makarantu Gabanin Azumi.” -Kwamishinan Harkokin Addinai

“Maslahar Al’umma Gwamnati Ta Duba Kafin Rufe Makarantu Gabanin Azumi.” -Kwamishinan Harkokin Addinai

by Mubarak Ibrahim Mandawari
0 comment

Kwamishinan harkokin addinai na jihar Kano Honorable Ahmad Tijjani Sani Lawal ya yi martani kan cece-kucen da ake yi game da rufe makarantu da wasu gwamanatocin Jihohi sukayi gabanin fara azumin watan ramadan.

Kwamishinan ya bayyana cewa an ɗauki matakin ne saboda maslahar al’umma, inda ya ƙara da cewa hakan zai bawa Mutane damar yin ibada, cikin kwanciyar hankali.

Honorable Ahmad ya bayyana hakan ne cikin wata ziyara daya kawo Gidan Rediyo da Talabijin na Muhasa a yau Laraba,”Gwamnati tana da ikon yin abubuwan da za su sauƙaƙawa al’ummarta indai basu saɓawa doka ba,”a cewar sa.

An sami cece-kuce da kuma mabanbantan ra’ayoyi tsakanin al’umma dama wasu jami’an gwamnati, inda suke sukar matakin rufe makarantun Firamare da Sikandire, inda wasu suke ganin hakan ya saɓawa tsari.

Cikin tattaunawar da yayi, ya roƙi  al’umma dasu dage tuƙuru wajen yin ibada, tare da saka shugabanni a cikin adduo’insu.

 

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?