Home » Matatar Dangote Ta Janye Karar Da Ta Kai NNPCL Kotu

Matatar Dangote Ta Janye Karar Da Ta Kai NNPCL Kotu

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar a gaban kotu kan hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur a Najeriya, NMDPRA da kamfanin man fetur na Najeriya NNPCL, da kuma wasu kamfanonin mai guda biyar.

Ƙarar da aka shigar ta nemi waɗanda ake ƙara da su biya diyyar naira biliyan 100.

Ƙarar dai ta zargi NMDPRA da bayar da lasisin shigo da man fetur ba bisa ka’ida ba, wanda Dangote ya ce ya saɓa da dokar masana’antar man fetur ta 2021.

Sauran kamfanonin da aka kai ƙara sun haɗa da AYM Shafa da A.A. Rano da T. Time Petroleum, 2015 Petroleum da kuma Matrix Petroleum.

Dangote ya buƙaci kotu ta bayyana cewa NMDPRA ba ta tallafa wa matatun cikin gida yadda doka ta tanada ba.

Sai dai waɗanda aka kai ƙara sun mayar da martani cewa suna da cikakken cancantar karɓar lasisin, kuma Dangote na ƙoƙarin neman mamaye kasuwar man fetur a Najeriya ne gaba ɗaya.

A wata takarda da lauyoyin Dangote suka gabatar a kotu, sun bayyana cewa kamfanin ya yanke shawarar janye karar, ba tare da bayyana dalili ba.

Babu tabbacin ko an cimma yarjejeniya a bayan fage.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?