Home » Matsalar Rashin Tsaro Na Neman Kassara Arewacin Najeriya– Ƙungiyar Tuntuba Ta Arewa

Matsalar Rashin Tsaro Na Neman Kassara Arewacin Najeriya– Ƙungiyar Tuntuba Ta Arewa

by Mubarak Ibrahim Mandawari
0 comment

Ƙungiyar Tuntuba Ta Arewa ta ACF, ta nuna damuwarta kan yadda matsalar rashin tsaro ke neman kassara yankin Arewacin Najeriya, Shugaban Kwamitin Amintattun ƙungiyar Alhaji Bashir Muhhamd  Ɗalhatu Wazirin Dutse ne ya bayyana hakan a yayin ziyarar da ƙungiyar takai jihar Borno.

Alhaji Bashir Ɗalhatu ya ƙara da cewa yanayin yadda ake samun ƙaruwar tashe-tashen hankula a yankin na Arewa abun tsoro ne.

ACF ta nemi mahukunta da su ɗauki matakan gaggawa da zasu kawo ƙarshen matsalolin tsaro da ya addabi yankin.

Matsalar tsaro a Arewacin Najeriya ita ce babbar barazana da take addabar yankin. Musamman Jihohin Sakkwato da Zamfara da Katsina.

A baya baya ne dai Ƙungiyar ta dattawan Arewa ta gudanar da wani taro a Kaduna inda aka haɗa kan manyan Arewacin Najeriya domin nemo bakin zare da mafita ga yankin.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?