Ƴan wasannin ƙasa Najeriya da suka shiga wasanni 12 a gasar ta Olympic da ke gudana a birnin Paris na ƙasar Faransa, ba su yi nasarar lashe wata lambar yabo ba.
Wannan dai na zuwa e ne bayan da duk ‘yan wasannin basu yi abun azo a gani ba a gasar.
Tuni dai Ministan Wasanni na Ƙasar, John Enoh ya bai wa ƴan Najeriya haƙuri game da wannann rashin katabus ɗin da tawagar yan wasannin tayi. kuma ya yi alƙawarin samun sauyi da jajircewa tsakanin ‘yan wasan.