Najeriya Na Rasa Kashi 20 Zuwa 30 Na Kudin Da Take Kashewa Kowace Shekara Saboda Rashin Gaskiya -FIDAC.

Babban Daraktan Cibiyar Ba da Shawarar Kuɗi da Ci Gaban Tattalin arziki (FIDAC), Dokta Abdulssalam Kani, ya ce bincike ya nuna cewa Najeriya na rasa kusan kashi 20 zuwa 30 cikin 100 na kudaden da take kashewa a kowace shekara saboda rashin gaskiya da rashin sa ido, da cin hanci.

Ya bayyana haka a wani taron kara wa juna sani ga ƙungiyoyin farar hula da kafafen yada labarai kan yadda ake sarrafa kasafin kuɗi na Jihar Kano. An gudanar da taron ne a ƙarƙashin shirin Wayar da Kai a kan Bin Doka da Yaƙar Cin Hanci (ROLAC II) tare da tallafin Ƙungiyar Tarayyar Turai.

Abokiyar aikinmu Zubaida Abubakar Ahmad na da cigaban wannan rahoton:

Post masu alaƙa

Rundunar ƴan sandan jihar Zamfara ta kama wanda ake zargi da safarar Alburusai a tankin Babur

‘Iran ta buɗe wa wani jirgi wuta a mashigar Hormuz

Ƙungiyoyin PDP 293 sun koma APC a Yobe