Najeriya za ta binciki kamfanonin sada zumunta na Meta, X da AI

Gwamnatin Najeriya ta ce za ta gudanar da bincike kan manyan kamfanonin fasaha na duniya da suka haɗa da Meta, X (Twitter), Alphabet da kuma wasu kamfanonin fasahar AI da ke aiki a Najeriya.

Hukumar kare haƙƙin masu amfani (FCCPC) ta ce binciken ya biyo bayan zarge-zargen karya dokokin amfani da ɗaukar bayanai daga kafafen yaɗa labarai ba tare da izini ba, da kuma wasu mu’amaloli da ake ganin na iya zama rashin adalci ga tsarin dijital a ƙasar.

Matakin ya biyo bayan umarnin da shugaban ƙasar, Bola Ahmed Tinubu, ya bayar ga hukumar FCCPC, domin ta duba wani korafi da ƙungiyar masu yaɗa labarai ta Najeriya, NPO ta gabatar wa fadar shugaban ƙasa.

Mataimakin shugaban FCCPC Mr. Tunji Bello, ya ce hukumar za ta gudanar da bincike na gaskiya bisa hujjoji, tare da tabbatar da cewa dukkan ɓangarori za su samu damar bayyana matsayarsu.

Post masu alaƙa

Za a kwaso ’yan Najeriya kusan 300 daga Afirka ta Kudu ranar Laraba

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta kama motoci marasa lamba 81 a Operation Clean Plates

Akwai haɗa bakin ƴan cikin gida a harƙallar hukumar bogi