• Home  
  • Nijeriya Da Saudiyya Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Tsaro Ta Shekaru 5
- Babban Labari - Labarai

Nijeriya Da Saudiyya Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Tsaro Ta Shekaru 5

Nijeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan sabuwar yarjejeniyar fahimtar juna ta shekaru biyar (MoU) don karfafa hadin gwiwar tsaro a tsakanin kasashen biyu. Yarjejeniyar, wacce aka sanar a ranar Talata a cikin wata sanarwa da Ahmed Dan Wudil, Mataimaki na Musamman kan Yada Labarai ga karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, ya fitar, ta bayyana […]

Nijeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan sabuwar yarjejeniyar fahimtar juna ta shekaru biyar (MoU) don karfafa hadin gwiwar tsaro a tsakanin kasashen biyu.

Yarjejeniyar, wacce aka sanar a ranar Talata a cikin wata sanarwa da Ahmed Dan Wudil, Mataimaki na Musamman kan Yada Labarai ga karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, ya fitar, ta bayyana cewa, hadin gwiwar ta shafi dabarun horar da sojoji, raba bayanan sirri, samar da tsaro, da ayyukan hadin gwiwa.

An sanya hannu a yarjejeniyar ne a Riyadh ta hannun Ministan Tsaro na Nijeriya, Matawalle, da Dr. Khaleed H. Al-Biyari na Saudiyya, ana sa ran yarjejeniyar za ta zama tsarin ci gaban tsaro mai dorewa a fadin kasashen biyu.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai