Home » NUC Ta Bankado Wasu Haramtattun Jami’o’in 49 a Nijeriya 

NUC Ta Bankado Wasu Haramtattun Jami’o’in 49 a Nijeriya 

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
NUC Ta Bankado Wasu Haramtattun Jami’o’in 49 a Nijeriya 

Hukumar kula da jami’o’in ƙasar nan (NUC) ta tona asirin wasu jami’oi 49 na kasar masu ba da takardar shaidar kammala Digiri na farko ba bisa ƙa’ida ba.

Waɗannan jami’oi 49 dai ba su da lasisi da gwamnatin tarayya. Don haka, hukumar na jan hankulan al’umma musamman iyaye da masu neman digiri na farko cewa, an rufe makarantun, sabida karya dokar harkar ilimi mai lamba CAPE3 ta Tarayyar Nijeriya (2004).

Matakin da NUC ta dauka kan wadannan haramtattun jami’o’i ya nuna aniyarta na tabbatar da ingancin tsarin ilimin Nijeriya.

Hukumar ta shawarci al’umma da su tabbatar da matsayin kowace jami’a tare da NUC kafin su fara karatu acikinta, ta yadda za su kiyaye kokarinsu na neman ilimi da makomarshi.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?