Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano Ta Haramta Wasan Tashe

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano ta sanar da dakatar da wasannin tashe watan Azumi wanda aka fi a cikin ƙwayar birnin kano.

Wannan umarni ya fito ne ta bakin kakakin rundunar ‘yan sanda reshen jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, wanda ya sanar da hakan.

A cewarsa, dalilin haramta wasan tashen shi ne akan samu wasu da kai yi basaja a matsayin masu tashen wajen aiwatar da mugayen laifuka kamar ƙwacen wayar hannu da shan miyagun ƙwayoyi da makamantansu.

Inda ya tabbatar da cewa; duk wanda aka kama da saɓawa wannan doka, to tabbas doka za ta yi aiki a kansa.

Sannan hukumar ‘yan sandan ta ƙara tabbatar da hana dokar kilisa ba tare da bin ƙa’idar da aka tanada ko kunna abubuwan fashewa da aka fi sani da Knock-out.

Su ma ya tabbatar da cewa duk wanda aka kama da wannan laifi to zai ɗanɗana kuɗarsa.

Post masu alaƙa

Barista Hamza Ɗantani ya jinjinawa CP Bakori da wasu kwamishinonin yan sanda biyu.

Rundunar yan sandan jihar Kano ta ceto fasinjoji 9 bayan musayar wuta da yan bindiga a hanyar Doguwa.

Kwalejin Fasaha ta Kogi ta dakatar da lakcarori 7 kan cin zarafin ɗalibai