Home » Sarkin Kano Na 14, Muhammadu Sanusi II, Ya Yaba Wa Shugaba Tinubu Kan Cire Tallafin Mai

Sarkin Kano Na 14, Muhammadu Sanusi II, Ya Yaba Wa Shugaba Tinubu Kan Cire Tallafin Mai

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Sarkin Kano Na 14, Muhammadu Sanusi II, Ya Yaba Wa Shugaba Tinubu Kan Cire Tallafin Mai

Sarkin Kano na 14, Muhammadu Sanusi II ya yaba wa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa janye tsarin tallafin man fetur da kuma fatali da bambanci wajen farashin kudin ƙasashen ƙetare.

Sanusi II ya bayyana matsayarsa ne a yayin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan ganawarsa da Mai girma shugaban kasa a jiya Alhamis.

Muhammadu Sanusi ya bayyana shugaba Tinubu a matsayin abokinsa wanda ya ce ya kama hanyar gyara kasa, wanda a dalilin hakan ne ma ya kawo masa ziyara.

Dayake bayani, Sunusi Lamido yace, kamar yadda aka san abubuwan da su ke magana a kai: tallafin man fetur ya zama ala-ƙa-ƙai, haka ma bambancin farashin kudin kasar waje da sauransu.

Ya ƙara da cewar, wadannan su ne abubuwan da ya ke magana a kai na tsawon lokaci, kuma ya yi farin ciki da shugaban ƙasa ya taɓo su.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?