Sarkin Musulmi ya bayyana sabon kiyasin kudin zakka, sadaki da diyyar rai

A dai dai lokacin da ake tsaka da gudanar da bukukuwan babbar Sallah Mai alfarma Sarkin Musulmi ya fitar da sanarwar nisabin Zakkah, da Sadaki da Diyyar rai.

A sanarwar da sarkin Musulmin ya fitar, wacce hukumar kula da ganin jinjirin wata ta yada a shafinta na Facebook ta ce, yanzu nisabin Zakkah ya koma naira miliyan 3 da dubu dari 918 da dari 800…… (N3,918,800,)

Sai Diyyar rai wanda kudin ya kama naira miliyan N195 da dubu 940,000, duba da darajar kudade da ake dasu a yanzu.

A bangaren haddin sata da sadakin aure kuwa, mafi ƙaranci shine N48,985.

Wannan kaɗan kenan daga cikin hanyoyin da addinin Islama ya tanada don yiwa kowa adalci a fannin gudanar da rayuwar yau da kullum.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr