Sarkin Musulmi ya bayyana sabon kiyasin kudin zakka, sadaki da diyyar rai

A dai dai lokacin da ake tsaka da gudanar da bukukuwan babbar Sallah Mai alfarma Sarkin Musulmi ya fitar da sanarwar nisabin Zakkah, da Sadaki da Diyyar rai.

A sanarwar da sarkin Musulmin ya fitar, wacce hukumar kula da ganin jinjirin wata ta yada a shafinta na Facebook ta ce, yanzu nisabin Zakkah ya koma naira miliyan 3 da dubu dari 918 da dari 800…… (N3,918,800,)

Sai Diyyar rai wanda kudin ya kama naira miliyan N195 da dubu 940,000, duba da darajar kudade da ake dasu a yanzu.

A bangaren haddin sata da sadakin aure kuwa, mafi ƙaranci shine N48,985.

Wannan kaɗan kenan daga cikin hanyoyin da addinin Islama ya tanada don yiwa kowa adalci a fannin gudanar da rayuwar yau da kullum.

Post masu alaƙa

Manjo Janar Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Yan Bindiga

JIBWIS Gwallaga Sun Ziyarci A Sansanin Alhazai Na Jihar Bauchi Domin Bada Agaji

‘Yan Arewa A Jihohin Kudu Sun Koka kan Tsangwama da Wariya Saboda Matsalolin Tsaro