• Home  
  • Sashen Lura da Basussukan Najeriya, DMO, ya ja hankalin shugaba Tinubu game da ciwo bashi
- Labarai

Sashen Lura da Basussukan Najeriya, DMO, ya ja hankalin shugaba Tinubu game da ciwo bashi

Haka zalika hukumar ta yi kira ga gwamnatin tarayya ta nemi hanyoyin da za tayi wajen ganin ta kara samun kudin shiga a cikin lalitar ƙasar nan.

Sashen Lura da Basussukan Najeriya, DMO, ya ja hankalin Tinubu game da ciwo bashi

Sashin lura da al’amuran bashi a Najeriya DMO, ya gargadi gwamnatin tarayya game da ƙarin karbo aron kudi a irin halin da ake ciki.

 Inda ya ce, an fadawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya zama dole ya gujewa cin bashi a yanzu.

Hukumar ba ta goyon bayan cin bashin ganin cewa kashi 73.5  na kudin shigar da za a samu a bana duk zai tafi ne a wajen biyan bashin da aka karbo.

Haka zalika hukumar ta yi kira ga gwamnatin tarayya ta nemi hanyoyin da za tayi wajen ganin ta kara samun kudin shiga a cikin lalitar ƙasar nan.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai