Saudiyya za ta zuba jarin biliyoyin Dala a Siriya

Saudiyya ta sanar da wani gagarumin zuba jari a fannin samar da ababen more rayuwa a Syria, a yayin da ta ke jaddada goyon bayanta ga gwamnatin Damascus.

Ƙasar Saudiyyar ta sanya kuɗin da ya kai dala biliyan biyu wajen gina sabbin filayen tashi da saukar jirage biyu a birnin Aleppo, da kuma dala biliyan ɗaya domin inganta harkokin sadarwa na zamani a Syria.

Akwai kuma wasu kuɗaɗen da za a sanya a fannin makamashi, da gina gidaje, da kuma samar da sabon kamfanin jirgin sama.

Gwamnatin Saudiya ta goya wa shugaban Syria Ahmed Al-Sharaa baya, tun bayan da ya maye gurbin hamɓararren shugaba Bashar Al Assad a ƙarshen shekarar 2024.

Post masu alaƙa

Yan sanda sun kama mutane 79 tare da kwato kwayoyi da makamai a bikin Takutaha a Kano.

Yan sanda sun kama wanda ake zargi da damfarar masu neman aikin gwamnati Naira miliyan 40.

Sabuwar majalisar gudanarwa ta POLAC za ta mayar da hankali kan inganta da ilimi da horo.