Saudiyya za ta zuba jarin biliyoyin Dala a Siriya

Saudiyya ta sanar da wani gagarumin zuba jari a fannin samar da ababen more rayuwa a Syria, a yayin da ta ke jaddada goyon bayanta ga gwamnatin Damascus.

Ƙasar Saudiyyar ta sanya kuɗin da ya kai dala biliyan biyu wajen gina sabbin filayen tashi da saukar jirage biyu a birnin Aleppo, da kuma dala biliyan ɗaya domin inganta harkokin sadarwa na zamani a Syria.

Akwai kuma wasu kuɗaɗen da za a sanya a fannin makamashi, da gina gidaje, da kuma samar da sabon kamfanin jirgin sama.

Gwamnatin Saudiya ta goya wa shugaban Syria Ahmed Al-Sharaa baya, tun bayan da ya maye gurbin hamɓararren shugaba Bashar Al Assad a ƙarshen shekarar 2024.

Post masu alaƙa

Ƴan sandan Kano za su ƙara ƙaimi wajen amsa kiran gaggawa – CP Bakori

Masu Garkuwa Da Janar Rabe Na Neman A Sako ’Yan Bindigar Da Ke Hannun Gwamnati

Gwamna Namadi ya dakatar da hadimansa huɗu