Farfesa Sadiq Umar Abubakar Gombe ya zama sabon Shugaban Jam’iyyar SDP na Ƙasa.
An sanar da zaɓensa tare da sauran mambobin Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa (NWC) a ranar Asabar yayin babban taron jam’iyyar na ƙasa na shekarar 2026 da aka gudanar a Filin Wasa na Abubakar Tafawa Ɓalewa da ke Bauchi.
Sauran shugabannin da aka zaɓa sun haɗa da Dakta Olu Agunloye a matsayin Sakataren Jam’iyya na Ƙasa; Sanata Dokta Ugochukwu Uba a matsayin Mataimakin Shugaban Jam’iyya na Ƙasa mai kula da Shiyyar Kudu; Hajiya Mariam Maggie Batube a matsayin Ma’ajiya ta Ƙasa; da Barista Joseph Achille Abu a matsayin Sakataren Tsare-tsare na Ƙasa.
