• Home  
  • SERAP Za Ta Maka Buhari a Kotu Kan Ɓacewar Gangar Mai 149
- Labarai

SERAP Za Ta Maka Buhari a Kotu Kan Ɓacewar Gangar Mai 149

Kungiyar Sa-Ido Kan Sarrafa Tattalin Arziki Mai Zaman Kanta (SERAP) ta yi barazanar gurfanar da gwamnatin tarayya a gaban kotu, idan har ta gaza gudanar da bincike kan zargin ɓacewar sama da ganga miliyan 149 na danyen man fetur.

Kungiyar Sa-Ido Kan Sarrafa Tattalin Arziki Mai Zaman Kanta (SERAP) ta yi barazanar gurfanar da gwamnatin tarayya a gaban kotu, idan har ta gaza gudanar da bincike kan zargin ɓacewar sama da ganga miliyan 149 na danyen man fetur.

Kungiyar ta fito ƙarara ta yi wa shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, barazana ne a wata wasiƙa mai dauke da kwanan watan 22 ga Afrilu shekarar da muke ciki.

Ta bayyana cewa, tana bukatar gwamnati ta kafa kwamitin bincike na shugaban kasa da zai gaggauta gudanar da bincike kan wannan zargi.

Kungiyar ta kuma bukaci shugaba Buhari da ya tabbatar da hukunta duk wanda ake zargi da hannu wajen wawure dukiyar man ƙasar nan, tare da ƙwato duk dukiyoyin da suka wawure.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai