Home » Shettima Ya Fasa Zuwa Taron Ƙungiyar Ƙasashen Rainon Ingila

Shettima Ya Fasa Zuwa Taron Ƙungiyar Ƙasashen Rainon Ingila

by Mubarak Ibrahim Mandawari
0 comment

Mataimakin shugaban ƙasar Najeriya Kashim Shettima ya fasa zuwa taron da ƙungiyar ƙasashe rainon Ingila ta Commonwealth na shekarar 2024, da za’a gudanar a tsibirin Samoa.

Shettima ya fasa zuwa taron ne saboda matsalar da jirgin sa ya samu a lokacin da ya yada zango a ƙasar Amurka.

Mai magana da yawun shugaban ƙasa Bayo Onanuga ya ce a lokacin da jirgin ya yada zango a birnin New York, wani abu ya daki jirgin mataimakin shugaban kasar wanda yayi sanadiyyar lalata gilas ɗin direban jirgin.

Sanarwar ta ƙara da cewa tuni dai Shugaba Tinubu ya amince da tura tawagar ministoci, ƙarƙashin jagorancin ministan Muhalli, Abbas Lawal domin su wakilci Najeriya.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?