Home » Shugaba Buhari Ya Ƙaddamar da Aikin Haƙar Man Fetur a Jihar Nassarawa

Shugaba Buhari Ya Ƙaddamar da Aikin Haƙar Man Fetur a Jihar Nassarawa

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ƙaddamar da aikin haƙar rijiyar man fetur a ƙaramar hukumar Obi a jihar Nasarawa da ke Arewa ta tsakiyar ƙasar.

Ƙaddamar da aikin tona rijiyar zai sa kamfanin mai na ƙasar NNPC, ya fara tono man fetur daga jihar.

A cikin watan Nuwamban bara ne dai shugaban ƙasar Muhammadu Buhari ya ƙaddamar da aikin haƙo man fetur a yankin Kolmani da ke tsakanin jihohin Bauchi da Gombe a yankin Arewa maso gabashin ƙasar.

Yawancin man da ƙasar ke da shi dai tana haƙoshi ne daga yankin Niger Delta a kudu maso kudancin ƙasar.

Najeriya dai ta dogara ne da man fetur da take fitarwa a matsayin hanayar samun kuɗin shiga,

Duk kuwa da ƙoƙarin da gwamnatocin ƙasar ke yi na faɗaɗa hanyoyin samun kuɗin shiga ga ƙasar.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?