Shugaba Tinubu ya gargadi kasashen duniya kan sace wa Afirka albarkatun kasa

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gargadi manyan kasashen duniya game da ci gaba da sace albarkatun nahiyar Afirka.

Ya yi gargadin ne a jawabin da ya gabatar a wurin taron shugabannin Afirka da aka yi a Nairobi babban birnin Kenya ranar Lahadi.

Ya yi wannan jawabi ne a yayin da manyan kasashen duniya ke ci gaba da gogayya da juna domin yin tasiri a Afirka abin da masana ke gani wani bangare ne na tatsar albarkatun kasar nahiyar.

Shugaba Tinubu ya yi tir da wannan sabon tsari na neman gindin zama a Afirka, inda ya yi kira ga kasashen nahiyar su hada kai domin cimma manufa iri daya.

Post masu alaƙa

Babandede Ya Ziyarci Iyalan Hon. Laushi, Ya Ba Su Tallafi

Da Fulani Aka Kama da Wuraren ƙera Makamai a Filato, da War Haka Duniya ta Dauka:-Zagazola Makama

Gwamna Bala Mohammed ya canja sheka daga jam’iyar PDP zuwa jam’iyyar APM