Shugaban Najeriya mai ci a yanzu Bola Ahmed Tinubu ya bayyana sha’awarsa ta sake yin takarar shugabancin ƙasar a babban zaɓen 2027, bayan da ya sayi fom ɗin shiga takara a yau Talata.
Ɗan majalisa mai wakiltar Ikeja a majalisar Tarayya, kuma wanda ke jagorantar ƙungiyoyi da ke goyon bayan Tinubu, James Faleke ne ya sayi fom ɗin a madadinsa a Abuja, kan naira miliyan 100.
Sakataren tsare-tsare na jamiyyar APC, Suleiman Argungu ne ya miƙa fom ɗin bayan da aka ƙaddamar da soma sayar da fom ɗin neman yin takara ga dukkanin masu son tsayawa takara.
