• Home  
  • Shugaban Amurka Joe Biden Ya Hakura Da Takara
- Babban Labari - Kasashen Ketare - Labarai

Shugaban Amurka Joe Biden Ya Hakura Da Takara

Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya ce ya haƙura da neman takarar shugabancin ƙasar a wa’adin mulki na biyu da yake nema. 

Shugaban Amurka Joe Biden

Shugaban Amurka Joe Biden ya ce ya haƙura da takarar neman shugabancin ƙasar a wa’adin mulki na biyu.

Shugaba Biden ya bayyana hakan ne a wani takataccen jawabi da ya wallafa a shafinsa na X,  ya ce ya bar takarar ne domin ”masalahar jam’iyyarsa da kuma ƙasarsa”.

Ya bayyana shekaru uku da rabi da ya yi yana jagorantar Amurka, ƙasar ta samu gagarumin ci gaba.

”A yau Amurka na da ƙarfin tattalin arziki a duniya, mun kafa tarihi a fannin zuba jari domin sake gina ƙasarmu” in ji shi.

Shugaba Biden dai na fuskantar mummunar hamayya daga tsohon shugaban kasar da ya kayar Donald Trump.

A baya-baya nan dai ana ta kiraye-kirayen Biden din ya hakura sakamakon shekaru da yanayi na rashin lafiya da ake zargin sun bayyana a jikinsa.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai