Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Adamawa, Bathiya, Ya Nada Mace a Matsayin Shugaban Masu Rinjaye

Kakakin majalisar dokokin Jihar Adamawa, Honarabul Bathiya Wesley, ya nada Kate Raymond Mamuno, a matsayin shugabar masu rinjaye na majalisar.

Wesley, ya sanar da haka ne a zaman majalisar na ranar Litinin, ya kuma bayyana dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Maiha Jingi Belel, a matsayin mataimakin shugaban masu rinjayen. Haka kuma kakakin majalisar ya bayyana mamba mai wakiltar karamar hukumar Yola ta Arewa, Suleiman Umar Alkali, a matsayin shugaban marasa rinjayen majalisar ta takwas.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr