Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Adamawa, Bathiya, Ya Nada Mace a Matsayin Shugaban Masu Rinjaye

Kakakin majalisar dokokin Jihar Adamawa, Honarabul Bathiya Wesley, ya nada Kate Raymond Mamuno, a matsayin shugabar masu rinjaye na majalisar.

Wesley, ya sanar da haka ne a zaman majalisar na ranar Litinin, ya kuma bayyana dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Maiha Jingi Belel, a matsayin mataimakin shugaban masu rinjayen. Haka kuma kakakin majalisar ya bayyana mamba mai wakiltar karamar hukumar Yola ta Arewa, Suleiman Umar Alkali, a matsayin shugaban marasa rinjayen majalisar ta takwas.

Post masu alaƙa

Babandede Ya Ziyarci Iyalan Hon. Laushi, Ya Ba Su Tallafi

Da Fulani Aka Kama da Wuraren ƙera Makamai a Filato, da War Haka Duniya ta Dauka:-Zagazola Makama

Gwamna Bala Mohammed ya canja sheka daga jam’iyar PDP zuwa jam’iyyar APM