Rundunar ‘yan sanda na shirin janye jami’anta masu yi wa manyan mutane rakiya da tsaro

Rundunar ‘Yan sandan Najeriya ta sanar da shirin janye wasu jami’an ‘yan sandan da ke ba da kariya da kuma rakiya ga manyan mutane da nufin sake tura su aiki a kan tsaron kasa.

Sabon Sufeto-Janar ɗin ‘Yan Sandan Najeriya, Olukayode Egbetokun, ya ce, “Duk da cewa kare martabar manyan mutane ya kasance mafi muhimmanci, amma ya zama wajibi mu daidaita abubuwan da muka sa a gaba don magance matsalar tsaro da ke addabar al’ummar ƙasar baki ɗaya.

A farkon watan nan ne dai shugaba Bola Tinubu ya yi sauye-sauye a jami’an tsaron Najeriya inda ya nada sabbin kwamandojin jami’an tsaro da suka hada na rundunar sojin ƙasar baki ɗaya.

Post masu alaƙa

Za a miƙa ƴan Najeriya da ake zargi damfara zuwa Amurka

Kotun majistare ta fara sauraren shari’ar sojan gona mai mukamin CSP 

Rundunar yan sandan jihar Kano ta kama wanda ake zargi da damfarar mutane da cewa shi babban jami’in Dan sandan ne.