Home » SNB Ta Buɗe Ofis A Jihar Kano

SNB Ta Buɗe Ofis A Jihar Kano

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Daga Mujahid Wada Musa

Ƙungiyar Ma’aikatan Kafafen Yaɗa Labarai Ta Ƙasa SNB ta buɗe ofis a jihar Kano, a wani ɓangare na ci gaba da taron bitar kara wa juna sani na kwanaki biyu da tsangayar koyar da aikin Jarida ta jami’ar Bayero Kano tare da haɗin gwiwar ƙungiyar SNB suka shirya.

Da yake bude Sabon ofishin, shugaban ƙungiyar na kasa Farfesa Umaru Pate, ya ce sun buɗe ofishin ne don kara hada kan dukkan ma’aikatan Telebijin da Radio a kasa Baki daya.

Haka zalika kungiyar ta bayar da kyautar na’ura Mai kwakwalwa guda daya don gudanar da aiyukan kungiyar a Sabon ofishin.

Pate, ya kara da cewa duk Wanda yake aikin Jarida Koda ya Yi ritaya yakamata ya shiga cikin kungiyar domin shima ya zama mamba.

Shugaban ya ce kungiyar tafi Mai da hankali wajen horas da mambonin ta da kuma kara mu su fasaha, sakamakon chanje-chanjen da Ake Samu a Radio da Telebijin, Inda sabbin fasahohi da kayan aiki suke fito wa, Wanda ya zama wajibi ma’aikatan kafafen yada Labaran su fahimci haka.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?