Burkina Faso: Sojoji sun daƙile yunƙurin juyin mulki

Gwamnatin Mulkin Soji ta ƙasar Burkina Faso ta sanar da cewa ta yi nasarar daƙile wani yunƙurin juyin mulki da aka yi a ranar Talata.

Mai magana da yawun gwamnatin sojin, Rimtalba Jean Emmanuel Ouedraogo, ne ya bayyana hakan, inda ya ce jami’an da suka yi yunƙurin juyin mulkin kan kama da yawa daga cikinsu, sannan an tsunduma neman waɗanda suka tsere.

Sannan ana cigaba da bincike domin bankaɗo waɗanda suka kitsa juyin mulkin.

Rundunar sojin, ta ce wannan yunƙuri ba komai ba ne facce ƙoƙarin tsunduma ƙasar cikin wani mahuyacin halli.

A ranar 30 ga watan Satumbar shekarar 2022, Kaftin Ibrahim Traoré, ya karɓe iko bayan wani juyin mulki da ya yi ƙasa da watanni takwas da wani juyin mulki da ya kaow ƙarshen mulkin dimokraɗiyya a ƙasar.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr