Rundunar sojin ƙasan Najeriya ta ce jami’anta sun samu nasarar tseratar mutum 23, waɗanda ta ce matafiya ne da ƴanbindiga suka tare a babbar hanyar Ayegunle zuwa Bunu da ke jihar Kogi, kamar yadda jaridar Guardian mai zaman kanta ta ruwaito a ranar Asabar 6 ga Yuni.
Rahotanni sun bayyana cewa ƴanbindiga sun tare hanyar ne domin sace mutane, amma sojoji suka kai agajin gaggawa bayan sun samu kiran kar-ta-kwana, inda suka isa wajen cikin lokaci suka fatattaki ƴanbindigar tare da tseratar da matafiyan.
Rahoton ya ƙara da cewa maharan sun tsere da suka ga isowar sojoji, “amma duk da haka sojojin sun bi bayansu domin farautarsu a cikin dajin.”
Sai dai jaridar ta ruwaito cewa mutum biyu sun rasu harin, sannan wasu biyar sun samu rauni.