Abuja

Gwamnati ta maka El-Rufai a Kotu

Gwamnatin Tarayya ta maka Nasir El-Rufai, tsohon Gwamnan Jihar Kaduna a kotu, kan zargin kutsen intanet a layin sadarwar Mashawarcin Shugaban Kasa kan sha’anin Tsaro, Nuhu Ribadu. Hukumar Tsaro ta DSS ce ta shigar da kara gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, inda take tuhumar El-Rufai da laifuka uku masu alaka da kutsen intanet. […]

Read more

Ana zanga-zanga kan dokar gyaran zaɓe a Najeriya

An fara zanga-zanga a Abuja, babban birnin tarayya, yayin da jam’iyyun adawa da ƙungiyoyin farar hula da ƙungiyoyin kwadago ke zargin Majalisar Tarayya da tauye dimokuraɗiyya ta hanyar ƙin amincewa da ƙudirin da zai wajabta tura sakamakon zaɓe ta na’ura. Zanga-zangar ta ɓarke ne bayan da ‘yan majalisa suka ƙi amincewa da wani sashe na […]

Read more

Ƙungiyar ƙwadago ta buƙaci ma’aikatan Abuja su koma aiki

Ƙungiyar ƙwadago ta buƙaci ma’aikatan Abuja su koma bakin aiki bayan cimma matsaya da ministan babban birnin tarayya, Abuja, Nyesom Wike, biyo bayan taron sulhu da aka gudanar domin warware matsalolin da suka haifar da yajin aikin da ake yi. Taron ya gudana bisa jagorancin shugaban kwamitin majalisar dattawa na Abuja, Sanata Mohammed Bomoi. Sanarwar […]

Read more

Matashi ya kashe mutum 3 a masallaci a Abuja

Wani matashi ya kashe mutum uku a masallaci a yayin da suke jiran Sallar Asuba a yankin Gwarimpa das ke Babban Birnin Tarayya, Abuja. Matashin ya daɓa wa mai kula da masallacin da wasu mutum biyu wuƙa har lahira a yayin da suke jiran sallar ne a masallacin da ke Kado Bimko a shiyyar First […]

Read more