EFCC ta ƙwace gidajen Malami a Abuja

Jami’an Hukumar EFCC mai yaƙi da masu yi wa tattalin arziki zagon ƙasa sun yi wa gidajen tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami ƙawanya a wani yunkuri na ƙwace muhallin tsohon Babban Lauyan na Najeriya.

Tun dai a ranar Litinin da ta gabata ce jami’an EFCCn suka ka ziyarci wasu gidajen tsohon ministan da ke Maitama a Abuja, da zummar rufe bisa abin da suka bayyana a matsayin aiwatar da umarnin kotu.

Rahotanni sun nuna cewa jami’an EFCC sun je wuraren ne da safiyar ranar, inda suka sanya alamar hattara da haramta amfani da gine-ginen, duk da ƙorafin Malami kan sahihancin umarnin kotun da jami’an suka gabatar.

Malami ya ce umarnin kotun da aka bayar tun a ranar 6 ga Janairu, 2026 na wucin gadi ne na tsawon kwanaki 14 kacal, wanda a cewarsa ya riga ya ƙare, kuma ya ƙalubalanci matakin a gaban kotu.

Post masu alaƙa

Gwamnatin Jigawa ta kashe kusan naira biliyan bakwai (7) domin tallafa wa ma’aikata ta fuskar noma

Jami’an tsaro sun ceto ɗalibai da malaman da aka sace a Kogi

Hukumomin tsaro sun kama wanda ya kirkiri hukumar bogi a Nijeriya