Babban sufeton ƴansandan Najeriya Kayode Egbetokun ya sauka daga muƙaminsa.
Wata majiya daga fadar shugaban ƙasa ta shaida wa BBC cewa Kayode Egbetokun ya ajiye aikinsa ne a ranar Talata.
Har zuwa yanzu, rundunar ƴansandan ƙasar ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance ba kan lamarin.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake ta ce-ce-ku-ce game da makomar shugabancin rundunar, kodayake babu cikakken bayani a hukumance kan dalilin ajiye aikin.
A watan Yunin 2023 ne shugaban Najeriya Bola Tinubu ya sanar da Kayode Egbetokun a matsayin wanda yake son naɗawa muƙamin sufeta-janar na ƴansandan ƙasar, inda a ƙarshen watan Oktoban shekara ta 2023 Majalisar ƴandsanda ta ƙasar ta tabbatar da nadin nasa.