Bola Tinubu

Shugaba Tinubu Ya Tafi Hutun Kwana 10 Kasashen Waje

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya fara wani hutun kwana 10 daga yau Alhamis, inda yake sa ran yin kwanaki a ƙasashen Turai irin su Faransa da Birtaniya. Hakan na ƙunshe ne a cikin wani bayani da mai magana da yawo shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ya fitar a yau Alhmais. Sanarwar ta ce “Shugaba Bola Ahmed […]

Read more

Shugaba Bola Tinubu Lafiyarsa Kalau – Gwamna Soludo

Gwamnan jihar Anambra, Farfesa Charles Soludo, ya ce ranar Litinin ya ziyarci Shugaban Kasa Bola Tinubu, kuma sabanin yadda ake ta rade-radi, shugaban na nan cikin koshin lafiya kuma babu abin da ke damun shi. A ’yan kwanakin nan dai ana ta samun jita-jitar cewa shugaba Tinubu na can kwance magashiyyan yana fama da rashin […]

Read more

Gwamnatin Tinubu Ta Mayar Da Arewa Saniyar ware – ACF

Kungiyar Tuntuba ta Arewa (ACF), ta yi korafin cewa Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Tinubu ta mayar da yankin saniyar ware a kasafin ayyukan raya kasar da take yi a yankin. Da yake jawabi yayin wani taron tattaunawa da ’yan kasa da Gidauniyar Tunawa da Ahmadu Bello ta shirya a Kaduna ranar Talata, Shugaban Kwamitin Amintattu […]

Read more

Tinubu Zai Karɓo Rancen $21bn Daga Ketare

Majalisar Dattawa ta amince da buƙatar Shugaba Bola Tinubu ta karɓo bashin ƙasashen waje da ya haura dala biliyan 21 domin aiwatarwa da cike giɓin kasafin kuɗin shekarar 2025 zuwa 2026. Majalisar ta bayyana cewa za a yi amfani da bashin ne wajen aiwatar da muhimman ayyukan ci gaban ƙasa, musamman a fannonin ababen more […]

Read more

Tinubu Ya sauya Sunan Jami’ar Maiduguri Zuwa Muhammadu Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami’ar Maiduguri zuwa Muhammadu Buhari, marigayi shugaban Najeriya. Tinubu ya sanar da haka ne a taron majalisar zartaswa da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja. “Kafin mu fara addu’o’i domin karrama Buhari, ina sanar da ku cewa mun sauya sunan Jami’ar Maiduguri zuwa Muhammadu Buhari,” in […]

Read more

Tinubu Zai Jagoranci Taron Yi Wa Buhari Addu’o’i A Abuja

Shugaban Najeriya Bola Tinubu zai jagoranci taron addu’o’i na musamman ga tsohon shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari a Abuja, babban birnin ƙasar. Cikin wata sanarwa da ma’aikatar yaɗa labaran ƙasar ta fitar ta ce taron – wanda za a gudanar da misalin ƙarfe biyar na maraice agogon ƙasar – zai samu halartar ministocin gwamnatin ƙasar. Bayan […]

Read more