Tinubu Ya Umarci Asibitocin Tarayya Su Rage Farashin Wankin Koda

Shugaba Bola Ahmed Tinubu

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya amince da rage farashin wankin ƙoda daga naira 50,000 zuwa naira 12,000 a manyan asibitocin tarayya a fadin ƙasar.

Daniel Bwala, mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan Bayanan da suka shafi tsare-tsaren gwamnati ne ya bayyana hakan a shafin sada zumuntansa na X, inda ya ce matakin zai sauƙaƙa wa dubban marasa lafiya masu fama da ciwon ƙoda.

An fara aiwatar da wannan mataki a manyan asibitoci kamar FMC Ebute-Metta da ke Lagos da FMC da ke Jabi a Abuja da UCH Ibadan da FMC Owerri da UMTH Maiduguri, yayin da za a ƙara wasu kafin ƙarshen shekara domin samun damar amfani da su a duk faɗin ƙasar.

Shugaba Tinubu a baya ya amince da haihuwa ta hanyar tiyata kyauta a asibitocin gwamnati domin inganta lafiyar mata da rage mace-macen da za a iya hana faruwarsu.

Post masu alaƙa

Tinubu Ya Sha Alwashin Ceto Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Oyo Da Borno

Kwamishinan ƴan sandan Kano, CP I.A. Bakori ya gargaɗi dakarunsa su guji shiga harkokin siyasa.

Alhazan Kebbi Rukunin Farko Sun Dawo Gida