Shugaba Tinubu Ya Tafi Hutun Kwana 10 Kasashen Waje

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya fara wani hutun kwana 10 daga yau Alhamis, inda yake sa ran yin kwanaki a ƙasashen Turai irin su Faransa da Birtaniya.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wani bayani da mai magana da yawo shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ya fitar a yau Alhmais.

Sanarwar ta ce “Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai bar Abuja yau, 4 ga watan Satumba domin fara hutu a Turai, a matsayin wani bangare na hutunsa na aiki na shekara ta 2025.

“Hutun zai ɗauki tsawon kwana 10.

“Shugaban kasar zai kwashe wani lokaci tsakanin Faransa da Birtaniya kafin ya koma ƙasar.”

Post masu alaƙa

Hadejia ta cika shekaru 120 da cin nasara kan turawan mulkin mallaka na Birtaniya.

NSCDC ta rufe wani gida da ake zargin ana safarar jarirai a Legos.

Rundunar ƴan sandan jihar Zamfara ta kama wanda ake zargi da safarar Alburusai a tankin Babur